DW Afrika ta rawaito cewa a wani sumame na hadin gwiwa da aka kai a yankin Accra na kasar, jami’an hukumar tsaron yanar gizo ta Ghana, ’yan sanda da hukumar shige da ficen kasar suka gudanar aka yi wannan kame.
Hukumomin sun bayyana cewa ana zargin mutanen da aikata laifuka da suka haɗa da damfara, zambar yanar gizo da satar kuɗade.
Haka kuma an kama wani ɗan kasar ta Ghana da ake zargin ya ba da hayar wajen zama ga kusan mutum 100 daga cikin waɗanda ake zargi.
