Friday, April 10, 2026
HomeUncategorizedCutar kwalara ta yi ajalin mutane 25 a Sokoto, yayin da...

Cutar kwalara ta yi ajalin mutane 25 a Sokoto, yayin da 15 ke kwance a asibiti

 

Cutar kwalara ta yi ajalin  mutane 25 a Sokoto, yayin da 15 ke kwance a asibiti

Akalla mutum 25 ne aka tabbatar da mutuwar su daga cikin  mutane 1,160 da su ka kamu da cutar Kwalara a jihar Sokoto. 

Kwamishiniyar lafiya ta jihar Asabe Balarabe, ta bayyana haka a ranar Litinin a lokacin da take zantawa da manema labarai.

Majiyar DCL Hausa wato Jaridar Punch, ta ambato kwamishiyiyar na cewa zuwa yanzu mutum 15 a ke ci gaba da kulawa da su a asibiti, a kananan hukumomin Sokoto ta Arewa da Silame da kuma Kware.

Yayinda gwamnatin jihar ke ci gaba da kokarin dakile yaduwar cutar, a cewar Hajiya Asabe Balarabe.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata