Rundunar sojin Nieriya ta ce ta dakile yunkurin harin ‘yan bindiga da suka yi kokarin shiga wasu al’ummomi a Shanono na Jihar Kano, bayan gumurzu mai tsanani da ya dauki tsawon lokaci.
Artabun ya fara ne a daren Alhamis zuwa wayewar Juma’a, inda aka gwabza fada a kauyukan Yankwada, Babanduhu da wasu makwabtansu a yankin.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga News Agency of Nigeria, kakakin rundunar sojin Nijeriya a Kano, Zubair Babatunde, ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi kokarin kutsawa kauyukan ne ta kan babura, suna harbe-harbe ba kakkautawa.
Babban jami’in ya kara da cewa harin ramuwar gayya ne, biyo bayan asarar da ‘yan bindigar suka yi a makon da ya gabata, lokacin da sojoji suka yi musu mummunan luguden wuta a wani artabu da suka yi da su.

Comment:Allah yakara karemu dakariyarsa, yakara shiga tsakanin nagari damugu.