Monday, April 6, 2026
HomeKetareGwamnatin Nijar ta rushe kungiyoyin agaji na NGO sama da dubu 1...

Gwamnatin Nijar ta rushe kungiyoyin agaji na NGO sama da dubu 1 na ciki da wajen kasar

A cikin wani kudurin doka ne da ministan cikin gidan Nijar Janar Mohamed Toumba ya dauka na ranar 7 ga watan Janairun nan ya sanar da matakin na rushe sama da kungiyoyi masu zaman kansu dubu daya sakamakon rashin mika takardunsu na bayanan inda suke samun kudadensu da yadda suka kashe su.

A cikin kudurin, ministan ya ce, cikin sama da kungiyoyi 3,000 da aka kididdige a kasar baki daya, 1,809 ne kawai aka amince da su cigaba da ayyukansu a hukumance. Cikin su, 1,684 na cikin gida ne yayin da 125 na ketare ne.

A baya, ministan cikin gidan ya ja hankalin kungiyoyin tare da ba su wa’adin ajiye takardun nasu a ofishinsa

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata