Shugaban Kwamitin Shugaban Kasa kan Gyaran Haraji, Taiwo Oyedele, ya ce yana fuskantar barazanar halaka sakamakon rawar da yake takawa wajen aiwatar da sabbin tsare-tsaren haraji a Nijeriya.
Oyedele ya bayyana haka ne an Abuja, yana cewa gyaran haraji yana taba muradun wasu mutane, lamarin da ke jawo adawa da barazana.
Ya ce ana kuskuren fahimtar gyaran, inda mutane ke zaton ana kara haraji ne, alhali ana ragewa da daidaita tsofaffi.
Ya bukaci ’yan Nijeriya masu goyon bayan gyaran su fito su yi magana, yana mai cewa sabon tsarin, duk da radadinsa, ita ce hanya daya tilo ta gyara tsarin harajin da ya gaza.
