Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Kano ta dakatar da likitocin da suka manta almakashi a cikin...

Gwamnatin Kano ta dakatar da likitocin da suka manta almakashi a cikin marar lafiyar da ya zama ajalinta

Hukumar Gudanar da Asibitoci ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa rashin kulawa ne ya janyo mutuwar Aishatu Umar, mahaifiya mai yara biyar, a Cibiyar Abubakar Imam ta Urology, bayan an bar almakashi a cikin jikinta bayan tiyata.

Hukumar ta dakatar da ma’aikata uku da suka shafi lamarin daga aiki, sannan ta mika batun ga Kwamitin Kula da Ka’idojin Likitoci na Jihar Kano don bincike da hukunci.

Iyalan marigayiyar sun nuna bakin ciki, yayin da mutane da dama a shafukan sada zumunta suka nemi a hukunta wadanda suka yi sakaci da kuma yin gyara a harkar lafiya.

Hukumar ta yi ta’aziyya ga iyalan marigayiya tare da tabbatar wa jama’a cewa irin wannan sakaci ba za a lamunta ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata