Ministan yada labarai na Nijeriya, Mohammed Idris, ya yi kira ga tawagar Super Eagles da su kasance masu mayar da hankali da kwarin gwiwa yayin da suke shirin fuskantar Morocco a wasan kusa da karshe na gasar cin kofin Afirka (AFCON) a daren Laraba.
A jawabin da ya wallafa a shafinsa na X, Idris ya yaba da yadda tawagar ta taka leda a gasar, yana mai cewa kowane wasa da suka buga ya nuna ladabi, jarumta, da imani, wanda ke tuna dalilin da yasa Super Eagles ke daga cikin manyan kungiyoyi a Afirka.
Ya kara da cewa, suna dauke da tarihi mai daraja a gasar Afirka. Daga nasarorin baya a AFCON zuwa nasarori kan manyan abokan hamayya, suna daukar tutar Najeriya da alfahari a koyaushe. Idris ya yi kira da su buga wasan cikin hadin kai, kwarin gwiwa, da nufin nasara.
A karshe, ministan ya ce, “Ku fita ku rubuta wani sabon babi mai alfahari a tarihin kwallon kafarmu. Ku buga da zuciya, ku buga da alfahari, ku buga don Nijeriya. Allah ya taimaka muku, Super Eagles. Allah ya taimaki Nijeriya.”
