Monday, April 6, 2026
HomeWasanniGwamnatin Nijeriya ta karfafi tawagar Super Eagles da kalaman kwarin guiwa gabanin...

Gwamnatin Nijeriya ta karfafi tawagar Super Eagles da kalaman kwarin guiwa gabanin wasansu da Morocco a wasan kusa da karshe na AFCON

Ministan yada labarai na Nijeriya, Mohammed Idris, ya yi kira ga tawagar Super Eagles da su kasance masu mayar da hankali da kwarin gwiwa yayin da suke shirin fuskantar Morocco a wasan kusa da karshe na gasar cin kofin Afirka (AFCON) a daren Laraba.

A jawabin da ya wallafa a shafinsa na X, Idris ya yaba da yadda tawagar ta taka leda a gasar, yana mai cewa kowane wasa da suka buga ya nuna ladabi, jarumta, da imani, wanda ke tuna dalilin da yasa Super Eagles ke daga cikin manyan kungiyoyi a Afirka.

Ya kara da cewa, suna dauke da tarihi mai daraja a gasar Afirka. Daga nasarorin baya a AFCON zuwa nasarori kan manyan abokan hamayya, suna daukar tutar Najeriya da alfahari a koyaushe. Idris ya yi kira da su buga wasan cikin hadin kai, kwarin gwiwa, da nufin nasara.

A karshe, ministan ya ce, “Ku fita ku rubuta wani sabon babi mai alfahari a tarihin kwallon kafarmu. Ku buga da zuciya, ku buga da alfahari, ku buga don Nijeriya. Allah ya taimaka muku, Super Eagles. Allah ya taimaki Nijeriya.”

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata