Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiKotu a jihar Kano ta bulale wani mutum ta kuma tura shi...

Kotu a jihar Kano ta bulale wani mutum ta kuma tura shi Islamiyya don koyon ilmin addini

Kotun Shari’ar Musulunci ta Jihar Kano da ke Kofar Kudu ta yankewa wani mutum mai suna Khalifa Auwal hukuncin aikin al’umma na tsawon watanni shida, bayan samunsa da laifin shiga gona ba da izini ba da kuma sata.

Lauyan gwamnati ya shaida wa kotu cewa an kama Auwal ne a yayin da yake yanke sandunan karfe a wurin aikin ginin gadar Tal’adu da ke Karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano.

Wanda ake tuhumar ya amsa laifukan da ake masa a gaban kotu. A hukuncinsa, Alkali Shamsuddeen Ado Abdullahi Unguwar Gini ya umarci a yi wa Auwal bulala 50 tare da ɗaure shi da aikin al’umma na tsawon watanni shida.

Alkalin ya kuma bayar da umarnin cewa Auwal ya yi karatun fikihu a makarantar Islamiyya karkashin kulawar Audu Dan Hajiya, wani jami’in kotu, a matsayin wani bangare na gyaran tarbiyyarsa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata