Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiTarayyar Turai ta cire Nijeriya daga jerin ƙasashen da ke da haɗarin...

Tarayyar Turai ta cire Nijeriya daga jerin ƙasashen da ke da haɗarin hada-hadar kuɗi

Tarayyar Turai (EU) ta sanar da cire Nijeriya daga jerin ƙasashen da ake kallon suna da haɗarin aikata laifukan kuɗi, a karkashin tsarin yaki da halatta kudaden haram (AML) da kuma dakile tallafawa ta’addanci (CFT).

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da Hukumar Nigeria Financial Intelligence Unit (NFIU) ta fitar, inda ta ce dokar Tarayyar Turai mai lamba EU C (2025) 8460, wadda aka amince da ita a ranar 4 ga Disamba, 2025, ta yi daidai da sabbin matakan da Kungiyar FATF ta dauka a taronta na Oktoba 2025.

Sanarwar ta ce wannan mataki zai fara aiki daga ranar 29 ga Janairu, 2026, inda aka kuma cire kasashen Burkina Faso, Mali, Mozambique, Afirka ta Kudu da Tanzania daga jerin, bayan da suka cika sharuddan da FATF ta gindaya wajen gyara matsalolin da aka gano a fannin yaki da safarar kudaden haram da tallafawa ta’addanci.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata