Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Kano ta musanta rahoton dakatar da harkokin mulki

Gwamnatin Kano ta musanta rahoton dakatar da harkokin mulki

Gwamnatin Jihar Kano ta musanta rahotannin da ke ikirarin cewa wani umarni daga Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dakatar da harkokin gudanar da mulki a jihar.

A cikin wata sanarwa da Sakataren yada labarai na Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG), Musa Tanko Muhammad, ya fitar, gwamnatin ta ce umarnin da aka bayar na wucin gadi ne kuma na kariya, wanda aka dauka bisa ka’idojin kudi da bin doka.

Sanarwar ta bayyana cewa umarnin, wanda ya dakatar da mikawa gwamna wasu fayil-fayil na wani dan lokaci, an bayar da shi ne a karshen watan Disamba, lokacin da kasafin kudin 2024 ya kare, yayin da kuma kudirin kasafin kudin 2025 ke gaban Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Gwamnatin ta jaddada cewa matakin bai shafi gudanar da ayyukan yau da kullum na gwamnati ba, tare da tabbatar wa al’umma cewa harkokin mulki a jihar na ci gaba da tafiya yadda ya kamata.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata