Monday, April 6, 2026
HomeKetareAna bikin cika shekaru 100 da maida birnin Yamai a matsayin babban...

Ana bikin cika shekaru 100 da maida birnin Yamai a matsayin babban birnin ƙasar Nijar

Hukumomin ƙasar Nijar, ƙarƙashin jagorancin Ministan Harkokin Cikin Gida, Janar Mohamed Toumba, ne suka shirya bikin tunawa da cikar Yamai shekaru 100 da zama babban birnin ƙasar.

A baya dai birnin Zinder ne ke matsayin babban birnin Nijar, kafin a shekarar 1926 lokacin mulkin mallaka, Turawa suka mayar da fadar gwamnatin ƙasar zuwa Yamai.

An gudanar da wannan biki ne a babban ɗakin taro na ƙasa da ƙasa da ke birnin Yamai, inda manyan jami’an gwamnati suka halarta, ciki har da ministoci da sauran manyan masu ruwa da tsaki a gwamnatin Janar Abdourahamane Tiani.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata