Bankin Duniya ya zai bayar da rancen dala miliyan 12 ga wasu jihohin Nijeriya da ke da sansanonin ‘yan gudun hijira, domin inganta tattara bayanai da cike gibin bayanan da suka shafi matsalolin gudun hijira.
Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa, an amince da bayar da kudin ne a karkashin wani sabon shiri wanda Bankin Duniya ya amince da shi a ranar 7 ga Agusta, 2025.
Rahoton ya bayyana cewa, kudin na daga cikin rancen dala miliyan 300 da International Development Association (IDA) ta amince da shi, wanda aka sanya hannu tsakanin Gwamnatin Nijeriya da Bankin Duniya,amma jihohi za su samu kudin ne kawai idan sun cika sharuɗɗan da aka shimfiɗa.
