Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta tabbatar da cewa an sace fiye da Kiristoci 100 daga Coci uku a jihar Kaduna, bayan da a baya ta musanta faruwar lamarin.
DW Afrika ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Lahadi a yankin Kurmin Wali, inda mazauna yankin suka ce adadin wadanda aka sace ya kai 177, sai dai mutane 11 sun samu damar tserewa daga hannun masu garkuwa da mutanen.
A cewar rundunar ‘yan sanda, musantawar da ta yi tun da farko ta faru ne sakamakon rashin samun bayanai, inda binciken da aka gudanar daga baya ya tabbatar da cewa an yi garkuwa da masu ibadar.
