Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiKotu ta bayar da belin Kwamishinan kuɗi na jihar Bauchi wanda ake...

Kotu ta bayar da belin Kwamishinan kuɗi na jihar Bauchi wanda ake zargi da tallafa wa ta’addanci

Kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da beli na Kwamishinan kuɗi na jihar Bauchi, Yakubu Adamu, da sauran wadanda ake tuhuma tare da shi, kan zargin tallafa wa ta’addanci da kudi dala miliyan 9.7.

Gidan talajibin TVC ya rawaito Mai shari’a Muhammad Umar ya amince da bukatar bayarda belin a Larabar nan, 21 ga Janairu, 2026, inda ya gindaya sharuddan da dole wadanda ake tuhuma su cika kafin su fita.

Kotu ta umurci kowane daga cikin wadanda ake tuhuma da ya gabatar da masu tsaya masa biyu, wadanda dole ne su kasance Babban Sakataren Ma’aikatar gwamnatin tarayya ko kuma matsayin Darakta a aikin gwamnati.

Haka kuma, an umurce su da su mika fasfo dinsu na kasa da kasa ga rajistaran kotu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata