Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiMa'aikatan KEDCO sun tsunduma yajin aiki

Ma’aikatan KEDCO sun tsunduma yajin aiki

Ƙungiyar manyan ma’aikatan wutar lantarki da ma’aikatan kamfanin rarraba hasken wutar lantarki na KEDCO sun tsunduma yajin aikin sai baba ta gani.

 

Yajin aikin da suka faro shi a ranar Laraba 21 ga watan Janairun 2026, ya biyo bayan zargin da suka yi na rashin kyakkyawan tsarin aiki, baya ga rashin biya musu bukatunsu cikin wa’adin da suka diba.

 

Yajin aikin ya yi sanadiyyar jefa wasu yankuna a jihar Kano cikin duhun rashin lantarki, kamar yadda rahotanni suka tabbatar.

 

Jaridar Punch ta ambato wasu daga cikin jagororin ma’aikatan na jaddada bukatunsu na inganta yanayin aiki, da kuma biyan su tarin basuka da suke bi tun daga shekarar 2014.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata