Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiFubara ne jagoran APC a jihar Rivers, ba Wike ba — Daniel...

Fubara ne jagoran APC a jihar Rivers, ba Wike ba — Daniel Bwala

Mai ba Shugaba Tinubu shawara kan harkokin yada labarai Daniel Bwala, ya bayyana cewa Gwamna Siminalayi Fubara shi ne jagoran jam’iyyar APC a jihar Rivers, yana mai jaddada cewa tsohon gwamna Nyesom Wike ba ɗan APC ba ne.

Bwala ya bayyana hakan ne a gidan talabijin na Channels a ranar Alhamis, yayin da ake fama da rikicin siyasa a Rivers, wanda ya kai ga Majalisar Dokokin jihar ta fara yunkurin tsige Gwamna Fubara.

Ya ce matsayin shugaban APC a bayyane yake cewa Fubara ne jagoran APC a Rivers, ba Wike ba, Wike ba memba ne na APC ba, don haka ba shi da ikon magana a madadin APC.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata