Ministar Al’adu, Hannatu Musawa, ta ce APC na iya fuskantar matsala a zaben 2027 idan ta cire Musulmi dan Arewa daga tikitin Shugaba Bola Tinubu. Ta ce hakan zai jawo cikas musamman a jihohin Arewa masu rinjaye.
Musawa ta bayyana cewa siyasar Arewa na da zurfi, inda jama’a ke daukar zabe da muhimmanci. Ta ce cire Sanata Kashim Shettima ko sauya tsarin tikitin Musulmi da Musulmi na iya fusata masu zabe.
Ta kuma ce hadin gwiwar jam’iyyun adawa ba ta da karfi a halin yanzu, tana mai jaddada cewa APC na da yakinin za ta ci gaba da rike mulki a 2027.
