Da safiyar Lahadi, 1 ga Fabrairu, 2026, ’yan bindiga sun kai mummunan hari a karamar hukumar Agwara, ta jihar Neja, inda suka kone Ofishin ’yan Sanda suka kona wani ɓangare na cocin UMC, tare da sace aƙalla mutane biyar.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa maharan sun isa garin da misalin 3:40–4:00 na asuba, inda suka yi musayar wuta da jami’an tsaro kafin daga bisani su yi amfani da abubuwan fashewa suka kona ofishin ’yan sanda bayan sun ci karfin jami’an da ke wurin.
Bayan haka, maharan sun nufi cocin UMC, inda suka kona wani ɓangare, sannan suka bazu zuwa cikin al’umma suka sace akalla mutane biyar, yayin da tsoro ya mamaye mazauna, da dama suka gudun hijira.
