Faransa, Hadaddiyar Daular Larabawa da kuma Turkiyya ne kasashen da shugaba Tinubu ya je a tsakanin wannan lokaci, inda ya halarci taruka daban-daban, baya ga kulla yarjejeniya a fannoni da dama.
Sai dai shugaban ya fuskanci suka daga wasu kungiyoyin fararen hula da kuma jam’iyyun hamayya, wadanda suka ce bai kamata Tinubu ya shafe lokaci mai tsayi a waje ba, daidai lokacin da Nijeriya ke fuskantar kalubale a cikin gida.
Amma shugaban jam’iyyar APC na Nijeriya Farfesa Nentawe Yilwatda, ya ce duk wata yarjejeniya da Tinubu ya kulla, ta kasance wadda za ta amfani ‘yan Nijeriya ne da kuma samar musu da ci-gaba, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
