Jam’iyyar APC ta ce har yanzu kofarta a buɗe take ga jagoran NNPP Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, idan har ya yanke shawarar shiga cikinta.
Shugaban Jam’iyyar na Nijeriya Farfesa Nentawe Yilwatda ne ya bayyana hakan yayin wata hira da ya yi da gidan talabijin na Trust a ranar Lahadi, a daidai lokacin da ake ci gaba da rade radin sauya sheƙar Kwankwaso.
Farfesa Yilwatda ya ce ko da yake ba a fara wata tattaunawa kai tsaye da Kwankwaso ba a halin yanzu, APC za ta karɓe shi hannu bibbiyu idan ya zaɓi shigowa jam’iyyar.
