Majalisar Dattawan Nijeriya ta fara duba rahoton kudirin gyaran dokar zabe ta 2022 da ke gabanta.
A zaman wanda Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ke jagorantar zaman, ya zuwa yanzu, Majalisar ta amince da sashe na 1 zuwa na 22 na kudirin dokar.
