Majalisar Dattawan Nijeriya ta nuna matuƙar damuwa kan tabarbarewar tsaro a jihar Katsina, musamman a yankin Funtua, bayan hare-haren ’yan bindiga da suka yi sanadin mutuwar mutane akalla 35 cikin sa’o’i 24 a ƙananan hukumomi uku.
Majalisar ta yi wannan kira ne a zaman ta na ranar Laraba, 4 ga Fabrairu, 2026, inda ta bukaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta cika alkawarin kafa sabon sansanin soja a yankin, tare da gargadin kada a yi wata tattaunawa da ’yan bindigar da ke addabar al’umma.
