Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiShugaba Tinubu ya girke sojoji a Kwara bayan harin da aka kai...

Shugaba Tinubu ya girke sojoji a Kwara bayan harin da aka kai jihar

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ba da umarnin girke dakarun soji a Kwara bayan harin da ya hallaka mutane da dama a jihar.

 

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa Bayo Onanuga ya fitar, ya ce an girke dakarun ne domin zakulo wadanda suka kai harin, tare da hana afkuwar irin sa a nan gaba.

 

Kazalika ya nuna damuwa tare da yin Ala wadai da abin da ya kira ‘mummunan hari’ kan al’umma, baya ga bayyana maharan a matsayin marasa imani.

 

Harin da aka kai garin Woro a jihar ta Kwara, ya zo ne bayan wani sumame da sojoji suka kai a yankin cikin makon da ya gabata.

 

Tuni dai Gwamnan jihar Abdulrahman Abdulrazaq ya sha alwashin daukar matakin da zai kawo karshen ayyukan ta’addanci musamman a kan iyakokin Kwara da Neja.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata