Wata kotu a Nijeriya ta umurci Gwamnatin Birtaniya da ta biya fam miliyan 20 ga kowane iyali daga cikin iyalan ma’aikatan ma’adanai na kwal 21 da hukumomin mulkin mallaka suka kashe a shekarar 1949 a yankin kudu maso gabashin Nijeriya.
Hukuncin ya fito ne daga Mai Shari’a Anthony Onovo na babbar kotun jihar Enugu, wanda kuma ya umurci Birtaniya da ta nemi afuwar hukuma kan kisan gillar da aka yi wa ma’aikatan.
DW Afrika ta rawaito cewa an harbe ma’aikatan ne a wajen ma’adanai na kwal a Iva Valley a ranar 18 ga Nuwamba, 1949, yayin da suke zanga-zangar lumana kan mummunan yanayin aiki, bambancin albashi, wariyar launin fata, da kuma albashin da ba a biya su ba.
