Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiMagoya bayan Senegal 18, da aka tsare a Morocco sun fara yajin...

Magoya bayan Senegal 18, da aka tsare a Morocco sun fara yajin cin abinci gabanin shari’arsu

Magoya bayan kasar Senegal guda 18, da aka tsare a Morocco bisa zargin tayar da tarzoma yayin wasan karshe na AFCON da aka yi a watan da ya gabata, sun fara yajin cin abinci gabanin shari’arsu, a cewar lauyansu.

Lauya Patrick Kabou ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Juma’a cewa mutanen sun shafe lokaci tun 18 ga Janairu ba tare da an bayyana musu tuhume-tuhumen da ake yi musu ba, ranar da aka kama su bayan rikicin da ya biyo bayan wasan karshe da Senegal ta doke Morocco.

Kabo ya ce wadanda ake tsare da su sun koka da cewa ‘yan sanda sun yi musu tambayoyi da harshen Faransanci da Larabci, alhali harshen da suka iya shi ne Wolof, wanda shi ne yaren gargajiyarsu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata