Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiNoman watanni biyar ya lalace cikin sa’o’i 48 — Koken manoman  Tumatur...

Noman watanni biyar ya lalace cikin sa’o’i 48 — Koken manoman  Tumatur a Borno

Manoman tumatir a jihar Borno sun koka bayan noman da suka shafe kusan watanni biyar suna yi ya lalace cikin sa’o’i 48, sakamakon matsalolin ajiya bayan girbi da faduwar farashi.

Rahotanni sun nuna cewa wasu manoma na rasa kashi 50 cikin 100 ko fiye na amfanin gonarsu, musamman waɗanda suka karɓi rance domin noman rani.

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, manyan matsalolin sun haɗa da rashin rumbunan ajiya, rashin ingantattun hanyoyin sufuri, saurin lalacewar tumatir cikin makonni 2 zuwa 3 kacal, da kuma kwari irin su Tuta.

Manoman sun yi kira ga gwamnati da ta gaggauta shiga lamarin ta hanyar kafa masana’antun sarrafa tumatir, domin rage asarar bayan girbi da ceton manoma daga halin ƙuncin da suke ciki.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata