Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Kogi ta rufe kasuwanni da tashoshin mota saboda matsalar tsaro

Gwamnatin Kogi ta rufe kasuwanni da tashoshin mota saboda matsalar tsaro

Gwamnatin Jihar Kogi ta sanar da rufe wasu kasuwanni da tashoshin mota na ɗan lokaci a sassan Yankin Kogi ta Yamma, a wani mataki na ƙara tsaurara matakan tsaro domin fatattakar ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga da sauran masu aikata laifuka a jihar.

An bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa na jihar, Mista Kingsley Fanwo, ya fitar a ranar Lahadi, 8 ga watan Fabrairun 2026.

Fanwo ya ce rufe kasuwannin da tashoshin motar na daga cikin goyon bayan da gwamnatin jihar ke bai wa ayyukan samar da tsaro da ake gudanarwa, tare da haɗin gwiwar Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (ONSA) da kuma shugabannin hukumomin tsaro a jihar Kogi.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata