Dan gwagwarmaya a Nijeriya Omoyole Sowore ya ce kaso 90 na ‘yan majalisar dokokin kasar ba za su koma kujerunsu ba in har za a gudanar da zabuka cikin gaskiya.
Sowore ya bayyana haka ne a matsayin marokan cece-kucen da ya barke game da batun gyaran dokar zabe, musamman sashen da ke magana kan aikewa da sakamako ta hanyar amfani da yanar gizo.
Da yake tattaunawa da gidan talabijin na Channels cikin shirin safiya, Sowore ya zargi ‘yan majalisun da kin bullo da dokokin da za su tabbatar da sahihancin zabuka a kasar, domin suna tsoron rasa kujerunsu.
A cewar sa, hujjar da aka gabatar ta cewa rashin yanayin sadarwa mai kyau zai tilasta yin amfani da takardu, tana nuna gazawa wajen kokarin tabbatar da adalci.



