‘Yan majalisar dokokin Amurka biyar sun mika wani kuduri da ke bukatar kakaba takunkuman da suka hada da hana biza da kuma kwace kadarorin jagoran jam’iyyar NNPP Rabi’u Musa Kwankwaso, kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah da Kautal Hore.
Kudurin ya biyo bayan shirin gwamnatin Amurka na daidaita zargin da ta kira da matsi kan ‘yancin addinin Kiristoci a Nijeriya, kamar yadda Dailytrust ta ruwaito.
‘Yan majalisar sun yaba da matakin shugaban Amurka Donald Trump na sanya Nijeriya cikin kasashen da ke bukatar kulawa ta musamman.
A cewar su, akwai bukatar gwamnatin Trump ta yi amfani da dukkanin damar da take da ita wajen kawo karshen musgunawar da suka ce ana yi wa Kiristoci da sauran mabiya addinai daban-daban.
