Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiNijeriya ta sadaukar wajen samar da daidaito a Liberia - Lt. Gen....

Nijeriya ta sadaukar wajen samar da daidaito a Liberia – Lt. Gen. Waidi Shaibu

Babban hafsan sojin kasa na Nijeriya Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya ce gagarumar sadaukarwar da Nijeriya ta yi ne ya samar da daidaito da zaman lafiya a  Liberia, lokacin da kasar ke fama da yakin basasa.

Waidi Shaibu ya bayyana haka ne a Liberia yayin bikin tunawa da ‘yan mazan jiya na kasar, kamar yadda sashen hulda da jama’a na rundunar sojin Nijeriya ya bayyana cikin wata sanarwa.

A cewar sa, Nijeriya ce ta dauki kaso mafi tsoka na nauyin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar, a zamanin yakin.

Ya kuma jaddada kudurin gwamnatin Nijeriya wajen ci gaba da karfafa alaka da kasar musamman ta fuskar tsaro.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata