Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaTinubu zai je Kano ranar Litinin domin karbar Gwamna Abba cikin jam’iyyar...

Tinubu zai je Kano ranar Litinin domin karbar Gwamna Abba cikin jam’iyyar APC

Ana sa ran Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai isa Kano ranar Litinin domin karɓar Gwamna Abba Kabir Yusuf cikin jam’iyyar APC a wani gagarumin taro da za a yi a filin wasa na Sani Abacha Stadium da ke Kofar Mata.

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima da wasu gwamnoni na APC za su halarci taron da ake kallon a matsayin muhimmin gangamin siyasa a Arewa maso Yamma.

Shugaban APC na Kano, Alhaji Abdullahi Abbas, ya ce taron zai zama alamar karɓar Yusuf a hukumance cikin jam’iyya, yana mai cewa hakan babban ci gaba ne ga APC a Kano, wadda ake dauka a matsayin muhimmiyar cibiyar siyasa a Nijeriya.

Ya ce an kafa kwamitoci da dama domin tabbatar da tsaro da gudanar da taron ba tare da tangarda ba, ciki har da kwamitin tsaro mai mambobi 15 karkashin jagorancin Kanal Umar Malami, da kwamitin wurin taro karkashin Bala Mohd Gwagwarwa.

Sauran kwamitocin sun hada da na yada labarai da hulda da jama’a, na lafiya da tsafta, da kuma na ladabi da karɓar baki, tare da kafa kwamitin wayar da kai domin tabbatar da halartar jama’a da dama a taron.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata