Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiNijeriya na cikin kasashen da ke yawan daukar yara aikin soja -...

Nijeriya na cikin kasashen da ke yawan daukar yara aikin soja – MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana Nijeriya a cikin kasashe biyar da ke da mafi yawan daukar yara cikin kungiyoyi masu amfani da makamai, tana mai gargadin cewa matsalar yara a yankunan rikici na kara tsananta a duniya.

Wakiliyar MDD kan Yara da Rikici, Vanessa Frazier, ta ce a 2024 kadai an tabbatar da yara sama da 7,400 da aka dauka ko aka yi amfani da su a rikice-rikice kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Ta ce kasashen da abin ya fi kamari sun hada da Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo, Nijeriya, Somaliya, Syria da Myanmar, inda ta jaddada cewa kowanne adadi na wakiltar rayuwar yaro da aka lalata.

A Nijeriya musamman Arewa maso Gabas, dubban yara sun shiga halin kunci sakamakon rikicin ‘yan ta’adda, inda sace-sace da tilasta musu shiga kungiyoyin makamai suka zama ruwan dare.

Frazier ta bukaci a maida hankali kan kariya da ilimi tare da hukunta masu daukar yara, tana mai cewa kare yara ba zabin son rai ba ne, illa wajibi domin samar da zaman lafiya mai dorewa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata