Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiJonathan da Akume sun saba wa juna kan ka’idar shekarun shugabanci

Jonathan da Akume sun saba wa juna kan ka’idar shekarun shugabanci

Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya bukaci Afirka ta bai wa matasa damar shugabanci, yana mai cewa shekaru 25 zuwa 50 sun fi dacewa da juriya da kuzarin zamani, inda ya ambaci Murtala Muhammed da Yakubu Gowon a matsayin shugabannin matasa masu tasiri.

Sai dai Sanata George Akume, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu, ya jaddada cewa shugabanci ba ya ta’allaka da shekaru, sai da hangen nesa da kwarewa, inda ya ce tasirin shugaba na fitowa ne daga tunani da iya aiki.

A taron da aka yi don tunawa da cika shekaru 50 da kisan Janar Murtala Muhammed, tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya danganta koma bayan tattalin arzikin Nijeriya da sauya manufofi ba tare da dorewa ba, musamman shigo da shinkafa tun 1979.

Obasanjo ya yi kira ga Afirka da ta mayar da hankali kan gyare-gyare masu dorewa da karfafa samarwa domin samun ci gaba mai ma’ana.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata