Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiZanga-zangar kyamatar 'yan Arewa ta yi ajalin Hausawa 4 a Port Harcourt...

Zanga-zangar kyamatar ‘yan Arewa ta yi ajalin Hausawa 4 a Port Harcourt jihar Rivers

Kungiyar Hausawa mazauna Jihar Rivers ta bayyana cewa mambobinta hudu sun hadu da ajalinsu a yayin zanga-zangar da ta gudana a karshen makon da ya gabata, wadda aka ce ta shafi ‘yan Arewa a Kasuwar Oil Mill da ke yankin Rumuokwurusi a Port Harcourt.

Shugaban Kungiyar Hausawan Jihar Rivers, Alhaji Musa Saidu, ne ya bayyana hakan a ranar Talata lokacin da ya jagoranci wasu shugabannin Arewa zuwa kasuwar domin duba halin da ake ciki, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Ya kuma ce an wawashe tare da lalata shaguna da dama mallakin ‘yan kasuwar Arewa a lokacin tashin hankalin

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata