Fadar Shugaban kasa ce ta fitar da sanarwar inda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya mika sakon gaisuwa ga kiristoci da musulmi bisa fara azumin Lent da Ramadan a lokaci guda.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taya kiristoci da musulmi murnar fara azumin Lent da Ramadan, wadanda suka zo a rana guda a bana.
Ya ce lokutan ibadun suna tunatar da ‘yan kasa muhimmancin imani, sadaukarwa da kaunar juna, tare da bukatar zaman lafiya, hadin kai da addu’ar cigaban kasa.
Shugaban ya yi fatan darussa da albarkatun wadannan lokuta masu tsarki su dawwama a rayuwar al’umma.
