Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiTinubu ya taya kiristoci da musulmi murnar fara azumin Lent da Ramadana

Tinubu ya taya kiristoci da musulmi murnar fara azumin Lent da Ramadana

Fadar Shugaban kasa ce ta fitar da sanarwar inda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya mika sakon gaisuwa ga kiristoci da musulmi bisa fara azumin Lent da Ramadan a lokaci guda.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taya kiristoci da musulmi murnar fara azumin Lent da Ramadan, wadanda suka zo a rana guda a bana.

Ya ce lokutan ibadun suna tunatar da ‘yan kasa muhimmancin imani, sadaukarwa da kaunar juna, tare da bukatar zaman lafiya, hadin kai da addu’ar cigaban kasa.

Shugaban ya yi fatan darussa da albarkatun wadannan lokuta masu tsarki su dawwama a rayuwar al’umma.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata