Sojojin Nijeriya sun sanar da fara taron tantance yara da ‘yan uwan sojoji da suka rasu, a cikin wani shiri na bayar da tallafin ilimi na shekarar 2026.
A wata sanarwar rundunar sojin ta wallafa a shafin ta na X ranar Alhamis, an bayyana cewa tantancewar za ta gudana a dukkanin yankuna shida na Nijeriya tsakanin Fabrairu da Maris 2026.
Sanarwar ta bayyana cewa, shirin tallafin ilimi na daga cikin tsare-tsaren jin kai na Sojojin Nijeriya da nufin tabbatar da cewa yaran ma’aikatan da suka rasu suna samun ilimi a matakai na Firamare, Sakandare da Jami’a.



