Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiMataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya roki 'yan kasar da su rika...

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya roki ‘yan kasar da su rika sanya Tinubu cikin addu’o’insu

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya bukaci ‘yan kasar da su rika sanya Shugaba Bola Ahmed Tinubu a cikin addu’o’insu yayin da Musulmi ke gudanar da Ramadan, Kiristoci kuma ke azumin Lent.

A cikin wata sanarwa da mataimakinsa kan harkokin yaɗa labarai ya fitar, Shettima ya ce wannan lokaci mai tsarki na ibada ya kamata ya zama dama ta roƙon Allah ya bai wa Tinubu hikima, ƙarfi da hangen nesa domin tafiyar da al’amuran ƙasa yadda ya dace, musamman a wannan lokaci na sauye-sauyen manufofi da ƙalubalen shugabanci.

Ya jaddada cewa haɗuwar Ramadan da Lent a lokaci guda dama ce ta haɗa kai wajen yin addu’a domin shugabanci nagari, zaman lafiya da kwanciyar hankali.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata