Hukumar ICPC mai yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya ta kaddamar da Mataki na 8 na shirin bibiyar ayyukan mazabu da na sashen zartarwa a Jihar Katsina, inda ake sa ido kan jimillar ayyuka 39 da kudinsu ya kai naira biliyan 13.5 a yankunan sanatoci da mazabun tarayya na jihar.
A cewar hukumar, tawagar bibiyar ayyukan ta hada da manyan jami’ai daga hedikwata da ofishin Katsina.
Hukumar ta ce ana gudanar da aikin ne tare da hadin gwiwar Nigerian Institute of Quantity Surveyors da kafafen yada labarai domin tabbatar da inganci, amfani da kudi yadda ya dace, da bin ka’idojin ayyuka.
Tuni an duba ayyukan cibiyoyin lafiya a birnin Katsina, hanyoyi a Funtua da Kankia, da ayyukan samar da ruwa a Kurfi, Dutsin-Ma, Mashi da Dutsi. Haka kuma an bibiyi ayyukan makarantu a Kafur, Sandamu, Daura da Mai’Adua, tare da fitilun kan tituna na hasken rana da shirye-shiryen tallafa wa al’umma.
Hukumar ta ce shirin na gudana karkashin kulawar kwamishinan da ke kula da jihar Katsina, Mr Ludam S. Samuel, a wani yunkuri na kara habaka gaskiya da rikon amana a ayyukan gwamnati.



