Monday, April 6, 2026
HomeKetareOrano a shirye yake ya tattauna da gwamnatin sojan Nijar

Orano a shirye yake ya tattauna da gwamnatin sojan Nijar

Kamfanin hakar uranium na Faransa, Orano, ya bayyana cewa a shirye yake ya fara tattaunawa da hukumomin mulkin soja na Jamhuriyar Nijar domin lalubo mafita da sasantawa kan batutuwan da ke tsakaninsu.

Kamfanin ya ce yana da niyyar warware sabanin cikin lumana ta hanyar tattaunawa da mahukuntan Nijar, bayan takaddama da ta biyo bayan sauyin mulki da aka samu a kasar.

Orano na daya daga cikin manyan kamfanonin da ke hakar uranium a Nijar, kasar da ke cikin manyan masu samar da ma’adinan uranium a duniya.

Hukumomin Nijar dai sun dauki wasu matakai kan harkokin kamfanin tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi, lamarin da ya haifar da rashin jituwar da ke bukatar sasantawa tsakanin bangarorin biyu.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata