Monday, April 6, 2026
HomeKetareMasu zanga zanga a Sénégal na neman adalci ga dalibin Jami'ar Cheikh...

Masu zanga zanga a Sénégal na neman adalci ga dalibin Jami’ar Cheikh Anta Diop ta birnin Dakar da aka halaka

Masu zanga zangar da suka hada da magoya bayan jam’iyya mai mulki ta Pastef sun amsa kiran wata hadaka ce ta dalibai da ‘yan fafutikar farar hula domin yin Allah wadai da kalubantar cin zarafin da ‘yan sanda suke yi.

Kutsen da jami’an tsaron ‘yan sandan suka yi ɗakin kwanan daliban Jami’ar Cheikh Anta Diop da kuma wasu fayafayen bidiyo masu tayar da hankali da aka gani su ne suka harzuka ‘yan kasar wadanda da dama suka tsammaci bankwana da irin wadannan dabi’u tun bayan zuwan sabbin hukumomin kasar a shekarar 2024.

To sai dai babban mai shigar da kara na kasar ya ce dalibin Jami’ar Abdoulaye ba ya rasu ne sakamakon fadowa daga saman bene na hudu inda dakin shi yake a Jami’ar a lokacin da yake kokarin guje wa gobarar da ta tashi, amma masu zanga zangar na cewa dalibin ba zai yi yunkurin gudun ba idan jami’an tsaron ba su abkawa dakunan kwanan nasu ba.

A cewar kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International mutum 66 ne aka hallaka a cikin rikicin siyasa a kasar daga shekarar 2021 zuwa 2024 wani yanayi marar dadi da kasar ta samu kanta a tarihi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata