Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, gaban kotu ba, duk da an yi masa tambayoyi tsawon kwanaki uku kan zarge-zargen cin hanci da rashawa.
Daily Nigerian ta rawaito cewa, hukumar ta tsare El-Rufai a hannunta na tsawon kwanaki biyu, daga ranar 16 zuwa 18 ga Fabrairu, bisa zargin cin hanci da rashawa da ake yi masa.
Wata majiya daga cikin hukumar ta shaida wa NAN cewa haryanzu ana ci gaba da binciken tsohon gwamnan, shi ya sa ba a kai shi gaban kotu ba tukuna.
Majiyar ta ƙara da cewa EFCC ba za ta yi gaggawar shigar da ƙara a kotu ba kan zargin da ta ke yi, sai ta kammala cikakken bincike cikin ƙwarewa da bin ƙa’ida.
