Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dage sauraron shari’ar da ake yi wa tsohon Ministan Shari’a na Nijeriya, Abubakar Malami, da dansa Abdulaziz kan zargin tallafa wa ta’addanci zuwa ranar 10 ga Maris, 2026.
Dagewar ta biyo bayan bukatar shugaban masu gabatar da kararraki na Nijeriya, Rotimi Oyedepo, wanda ya ce an sauya shari’ar daga hannun DSS zuwa ofishinsa, don haka yana bukatar karin lokaci domin nazarin takardun karar.
Lauyan wadanda ake kara bai yi adawa da dagewar ba, amma ya bukaci kotu ta soke karar idan masu kara ba su fara gabatar da shaidu a ranar da aka sanya ba.
Mai shari’a Joyce Abdulmalik ta amince da dagewar tare da umartar masu kara su fara shari’a a ranar da aka kayyade.
