Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaDan takarar Gwamnan jihar Sokoto na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Sa’idu...

Dan takarar Gwamnan jihar Sokoto na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Sa’idu Umar ya fice daga jam’iyyar

Tsohon dan takarar gwamnan Jihar Sokoto a 2023 karkashin jam’iyyar PDP, Saidu Umar, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar, yana mai danganta matakin da rikicin shugabanci da ke ci gaba a matakin kasa.

Umar ya bayyana hakan ne cikin wasikar murabus da ya aika wa shugaban jam’iyyar a mazabarsa ta Sarkin Adar Kofar Atiku da ke karamar hukumar Sokoto ta Kudu. Ya ce sabanin shugabanci da kararraki a kotuna sun janyo rashin hadin kai da tabarbarewar harkokin jam’iyyar.

Ficewar tasa na zuwa ne kwanaki kadan bayan tsohon gwamnan jihar, Aminu Waziri Tambuwal, shi ma ya bar PDP, lamarin da ke nuna karin sauyin siyasa da ke faruwa a jihar. Duk da haka, Umar ya ce zai ci gaba da goyon bayan dimokuradiyya da ci gaban jihar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata