Tsohon dan takarar gwamnan Jihar Sokoto a 2023 karkashin jam’iyyar PDP, Saidu Umar, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar, yana mai danganta matakin da rikicin shugabanci da ke ci gaba a matakin kasa.
Umar ya bayyana hakan ne cikin wasikar murabus da ya aika wa shugaban jam’iyyar a mazabarsa ta Sarkin Adar Kofar Atiku da ke karamar hukumar Sokoto ta Kudu. Ya ce sabanin shugabanci da kararraki a kotuna sun janyo rashin hadin kai da tabarbarewar harkokin jam’iyyar.
Ficewar tasa na zuwa ne kwanaki kadan bayan tsohon gwamnan jihar, Aminu Waziri Tambuwal, shi ma ya bar PDP, lamarin da ke nuna karin sauyin siyasa da ke faruwa a jihar. Duk da haka, Umar ya ce zai ci gaba da goyon bayan dimokuradiyya da ci gaban jihar.
