Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiHukumar ba da agajin gaggawa a Nijeriya NEMA ta karbi 'yan kasar...

Hukumar ba da agajin gaggawa a Nijeriya NEMA ta karbi ‘yan kasar 147 da suka makale a Jamhuriyar Nijar

Hukumar ba da agajin gaggawa a Nijeriya NEMA ta karɓi ‘yan kasar 147 da suka dawo daga Jamhuriyar a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da ke Kano, a wani mataki na tallafawa ‘yan kasar da ke dawowa daga ƙasashen waje.

A wata sanarwa da ofishin NEMA na Kano ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Juma’a, hukumar ta ce ‘yan Nijeriya din sun iso daga birnin Niamey a ranar 5 ga Maris, 2026 da misalin karfe 12:19 na rana.

Sanarwar ta bayyana cewa an gudanar da aikin karɓar su ne tare da haɗin gwiwar wasu hukumomi da suka haɗa da Nigerian Red Cross Society, da kuma Nigeria Security and Civil Defence Corps.

Hukumar ta ce an gudanar da tantance bayanan mutanen da suka dawo a ranar 6 ga Maris, inda aka gano cewa cikinsu akwai maza manya 136, mata manya biyar, yara maza uku da kuma yara mata uku.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata