Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaZiyarar Tinubu zuwa Landan hanyace ta sabunta hadin gwiwar Birtaniya da Nijeriya

Ziyarar Tinubu zuwa Landan hanyace ta sabunta hadin gwiwar Birtaniya da Nijeriya

Yayin da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ke shirin kai ziyara birnin Landan na kasar Birtaniya, a wani mataki da ake kallon zai taimaka wajen karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da sadarwa, Sunday Dare, ya bayyana cewa ziyarar wata dama ce ta sake farfado da mu’amala mai karfi tsakanin kasashen biyu.

A wata rubutacciyar sharhi da ya fitar gabanin ziyarar, Dare ya ce Burtaniya na daga cikin kasashen yamma da suka fi fahimtar tsarin siyasa da cibiyoyin gwamnati na Najeriya tsawon lokaci.

Sai dai ya kara da cewa a wasu lokuta kasar Burtaniya na nuna kamar ta nesanta kanta idan aka fara yada wasu rahotanni ko zarge-zarge game da Najeriya a tattaunawar duniya.

Ya ce ana sa ran ziyarar za ta taimaka wajen karfafa tattaunawa da hadin kai tsakanin kasashen biyu kan muhimman fannoni kamar siyasa, tattalin arziki da tsaro.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata