Rundunar ‘yan sandan Abuja, babban birnin tarayyar Nijeriya ta sanar da cewa a ranar 3 ga Afrilu, 2026 da misalin karfe 12:30 na dare, jami’an Rapid Response Squad da ke sintiri a yankin Kwali sun gano wata mata mai tabin hankali da mace a bakin hanya a kauyen Kwaita.
A sanarwar da SP Josephine Adeh ta aike wa DCL Hausa, ta ce jami’ansu sun kai matar da jairiryarta Asibitin Kwali inda aka ba su kulawar lafiya kafin a sallame su cikin koshin lafiya, sannan aka mika su ga jami’in jin kai na karamar hukumar Kwali, Malam Sadiq Kwali.
