Tsohon ɗan takarar shugabancin Nijeriya a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bukaci ‘yan kasar kada su sake zaɓen Shugaba Tinubu, yana mai danganta hakan da gazawa wajen inganta wutar lantarki a ƙasar.
Obi ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya tuna cewa Tinubu ya yi alkawarin idan bai samar da wutar lantarki mai dorewa cikin shekaru huɗu ba, kada a sake zaɓensa.
Ya ce a halin yanzu alkawarin bai cika ba saboda samun wutar lantarki ya ragu daga sama da megawatt 4,000 a shekarar 2023 zuwa ƙasa da haka yanzu, yayin da kuma farashin lantarki ke karuwa sossai.
