Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa za shawo kan matsalar ta’addanci da rashin tsaro, yana mai jaddada kudirin gwamnatinsa na kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin ƙasar.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa Shugaban ya yi wannan bayani ne yayin ƙaddamar da filin jirgin sama na Gateway International Cargo Airport a jihar Ogun.
Tinubu ya bayyana cewa ƙarfafa tsaro na daga cikin manyan manufofin gwamnatinsa, tare da bunƙasa tattalin arziki da ayyukan more rayuwa.
Ya ce muhimmantar da harkar tsaro da haɗin gwiwar ƙasa baki ɗaya za su taimaka wajen murkushe barazanar hare-haren ‘yan ta’adda a faɗin kasar.
