Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiNijeriya za ta magance matsalolin tsaron da ke addabarta - Shugaba Tinubu

Nijeriya za ta magance matsalolin tsaron da ke addabarta – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa za shawo kan matsalar ta’addanci da rashin tsaro, yana mai jaddada kudirin gwamnatinsa na kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin ƙasar.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa Shugaban ya yi wannan bayani ne yayin ƙaddamar da filin jirgin sama na Gateway International Cargo Airport a jihar Ogun.

Tinubu ya bayyana cewa ƙarfafa tsaro na daga cikin manyan manufofin gwamnatinsa, tare da bunƙasa tattalin arziki da ayyukan more rayuwa.

Ya ce muhimmantar da harkar tsaro da haɗin gwiwar ƙasa baki ɗaya za su taimaka wajen murkushe barazanar hare-haren ‘yan ta’adda a faɗin kasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata