Ɗan marigayi tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, wato Yusuf Buhari, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai.
A cikin wata wasiƙa da aka ruwaito ya aike wa masu ruwa da tsaki a ranar 3 ga Afrilu, Yusuf ya ce yana da burin bayar da gudunmawa wajen inganta shugabanci da kawo ci gaba ga al’umma.
Tun da farko dai wasu jiga-jigan jam’iyyar APC sun nuna goyon bayansu gare shi domin tsayawa takarar wakilcin mazabar Daura/Sandamu/Mai’Adua.
Sai dai rahoton jaridar Daily Trust ya ambato wasu masu ruwa da tsaki a yankin sun nuna adawa da abin da suka kira yunƙurin kakabawa jam’iyya ‘yan takara, suna mai cewa za su ci gaba da bin tsarin dimokuraɗiyya na jam’iyyar.
