Rikicin shugabanci da ke addabar jam’iyyar ADC ya ƙara ɗaukar zafi, bayan wani ɓangare na jam’iyyar ƙarƙashin jagorancin Nafiu Bala Gombe ya gudanar da zanga-zanga a hedikwatar INEC da ke Abuja, yana neman a amince da shi a matsayin halastaccen shugabancin jam’iyyar.
Zanga-zangar ta samu halartar magoya bayansa, ciki har da ɗan majalisar dokokin jihar Kogi, Leke Abejide, da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar, inda suka yi kira ga hukumar zaɓe ta ƙasa da ta bi doka wajen warware rikicin shugabanci da ke cikin jam’iyyar.
